8 Oktoba 2015 - 18:13

Hukumomin shari'a na kasar Iran zasu gabatar da taron bita domin gano wadanda ke da hannu a hadarin Mina

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti(a.s)-abna-hukumomin shari'a na Iran da hadin kwiwar kungiyoyin sa kai zasu fara taron bita domin gano wadanda suka haddas hadarin Mina wanda yai sanadiyar rasa rayukan mutane da dama.
Zaman zai hada da wakilai na bankare daban daban wanda zasu binciki ummul haba isin hadarin Mina da kuma bukatar a hukunta duk wani mai hannun a ciki.
Taron zai kasance ranar asabar 10 ga watan oktobar da misalin karfe 10 na safe a zauren taro na shaikh murtaza ansari dake jami'ar Tehran.
Idan za a iya tunawa a taron hajjin da ya gudana bana sakamakon tutsetseniyar da ta faru a Mina wanda hakan tai sanadiyar rasa rayukan munane da jikkata wasu inda adadin su ya kusa kai 7000 daga cikin su akwai mutanen Iran 464.